Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na al-Quds al-Arabi cewa, a ranar Larabar da ta gabata ne gidan talabijin na kasar Sweden ya bayar da rahoton cewa, an gano kwafin kur’ani mai tsarki guda uku a birnin Karlskrona da ke lardin Belkinge, tare da rubuta musu barazanar kisa da cin mutunci.
A cewar rahoton, an bar daya daga cikin kur’ani a tashar motar, sannan an bar wasu kwafi biyu a wuraren taruwar jama’a.
Gudlaug Hilmarsdottir dan kungiyar musulinci ta Ronbih ya bayyana rashin jin dadinsa da wannan lamari tare da jaddada cewa kur’ani shi ne jagora ga rayuwar musulmi.
A baya-bayan nan ne dai kasashen Sweden, Denmark da Netherlands suka fuskanci wulakancin kur'ani mai tsarki da wasu masu ra'ayin mazan jiya karkashin jagorancin Rasmus Paludan, shugaban jam'iyyar masu tsattsauran ra'ayi ta Denmark suka yi.
Da yawa suna son sanyawa gwamnatin Sweden takunkumi saboda goyon bayan aikata irin wadannan laifuffuka a wannan kasa, da kuma bibiyar lamarin ta hanyar hukumomin shari'a na kasa da kasa.