Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Siddi Al-Balad cewa, Muhammad Al-Saati, kakakin kungiyar hadisai da mahardata kur’ani mai tsarki a kasar Masar, ya yi maraba da wannan kuduri tare da bayyana hakan a matsayin abin kwarin guiwa ga dukkanin ma’abota ilimin kur’ani. Akwai da'irar kur'ani fiye da 15,000 a Masar, masu mambobi 10,000.
A daya bangaren kuma shugaban cibiyar kula da kur'ani ta kasar Masar Sheikh Mohammad Hashad a lokacin da yake bayyana farin cikinsa da wannan aiki ya bayyana Sheikh Mahmoud Al-Kasht da Dr. Ahmed Naina da Sheikh Abdul Fattah Al-Tarouti a matsayin mafi muhimmanci. kuma manya-manyan jiga-jigan karatun kur'ani a kasar Masar da ma duniya baki daya.
Daga nan sai ya bukaci ministan harkokin kyauta na kasar Masar da ya ba da umarnin kammala gyare-gyaren dokar kungiyar da aka aike masa, ta yadda kungiyar za ta iya cika aikinta da kuma taka rawar da ta dace.
https://iqna.ir/fa/news/4116098