IQNA

Jarabawar kasa domin tantance matakin daliban makarantun kur'ani a kasar Aljeriya

17:05 - March 16, 2022
Lambar Labari: 3487059
Tehran (IQNA) Ma’aikatar kula da harkokin addini da wa’azi ta kasar Aljeriya ta sanar da gudanar da jarrabawar kasa domin tantance matakin daliban makarantun kur’ani.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al-Shorouk cewa, a wata sanarwa da ma'aikatar kula da harkokin kyauta ta kasar Aljeriya ta fitar, ta ce za a gudanar da gwajin matakin ne domin halartar gasar kur'ani mai tsarki ta kasar da za a yi a ranakun 17 da 18 ga watan Afrilun 2022 .

Takardun da ake bukata don wannan jarrabawar sun hada da takardar haihuwa, takardar haddar Alkur'ani da aka yi shekara 2, da hotuna guda biyu da kuma bukatu a rubuce wanda sai a gabatar da su kafin ranar 13 ga Afrilu.

Za a gudanar da wannan jarrabawar ne a tsakanin cibiyoyin kur'ani da makarantun Al-Boyerieh, Tizi Wazu, Batnah, Qastanineh, Mileh, Gholizan, Telmsan, Saeededeh, Sukra, Al-Aghwat, Tamnafst, An Saleh da Alizi.

 

 

https://iqna.ir/fa/news/4043505

captcha