IQNA

Taron Cika Shekaru 60 Da Kafa Makarantar Muslunci A Ghana

21:04 - July 30, 2017
Lambar Labari: 3481752
Bangaren kasa da kasa, an gudanar da zaman taro dangane da cikar shekaru 60 da kafa makarantar musunci ta farko a kasar Ghana.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, shafin yada labarai na

«citifmonline» ya bayar da rahoton cewa, malam Isa Abubakar babban daraktar cibiyar musulmin arewacin Ghana ya bayyana cewa, wannan taro yan ada matukar muhimmanci ga dukkanin al'ummar Ghana musamman ma musulmi daga cikinsu.

Ya ci gaba da cewa, makarantun muslunci suna fuskantar matsaloli a kasar musamman a cikin shekarun baya-bayan nan, inda malamai da suke koyarwa suke janye jikinsu, bisa hujjar karancin albashi.

Y ace wannan ya nuna cewa akwai bukatar yin wani garambawul a harjar tafiyar da makantun muslunci a kasar, ta yadda za su zama daidai da sauran makarantu ta fuskar inganci da kuma daukar nauyin jami'a da kuma malamai.

A lokutan baya cibiyoyin muslunci ne dai suke daukar nauyin makarantunci muslunci, amma daga bisani daukar nauyinsu da kuma tafiyar da su ya koma akan wuyan gwamnati, duk kuwa da cewa musulmi ne suke nauyin yin tsare-tsaren tafiyarwa.

3624549



Taron Cika Shekaru 60 Da Kafa Makarantar Muslunci A Ghana

Taron Cika Shekaru 60 Da Kafa Makarantar Muslunci A Ghana
captcha