Kamfanin dillancin labaran iqna, kamfanin dillancin labaran sputnik ya habarta cewa, mamban na Ansarullah kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su taimaka a aikace domin ganin tattaunawar sulhu da ake yi tsakanin bangarorin kasar Yemen, ta kai ga samun nasara.
Haka nan kuma ya kara da cewa; Masu yakar kasar Yemen sun hau kan teburin tattaunawa ne bayan da su ka sha kashi a fagen daga, don haka da akwai shakku akan tsarkin niyyar Amurka na kawo karshen yaki.
Dan tawagar tattaunawar na Ansarullah ya kuma bayyana cewa; A yanzu da aka shiga kwana na biyu ana tattaunawar ba za a iya cewa an cimma wata matsaya ta azo a gani ba.
A ranar shida ga watan nan na Disamba ne aka bude tattaunawar sulhu a tsakanin bangarorin da suke yaki da juna a kasar ta Yemen, a kasar Sweeden bisa shiga tsakanin Majalisar Dinkin Duniya.
Saudiyya ta shelanta yaki ne akan kasar Yemen tun a shekarar dubu biyu da sha biyar wanda kawo ya zuwa yanzu ya ci rayuka fiye da dubu sha uku yayin da wasu dubu dubatar suka jikkata.
Bugu da kari yakin ya lalata asibitoci da cibiyoyin shan magani na kasar, kamar kuma yadda ya jawo bullar yunwa da cutar kwalara.