Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Saut Al-Ameh cewa, kungiyar ISECO ta shirya wani biki na kasa da kasa a birnin Rabat fadar mulkin kasar Morocco, a daidai lokacin da sarki Mohammed na shida ya bude gidan tarihi na tarihin rayuwar annabci da wayewar Musulunci na kasa da kasa.
An gudanar da wannan baje kolin ne tare da halartar kungiyar Isesco da kungiyoyin Musulunci na duniya da kuma kungiyar malaman Muhalliah ta kasar Morocco, kuma manufarsa ita ce gabatar da sakon Musulunci cikin adalci, zaman lafiya, jin kai, hakuri, zaman tare da daidaitawa.
Wannan baje kolin ya kunshi manyan sassa da dama, daga cikinsu baje koli na kasa da kasa da gidan tarihi na tarihin Annabi a farkon lokaci na daya daga cikin muhimman sassa, wanda aka nuna a karon farko da fasahar 3D da fasahar da ke da alaka da sararin samaniya.